Sinopsis
Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Alumma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalinariziki, aladu da dai sauransu
Episodios
-
Ra'ayoyin masu saurare kan tasa ƙeyar 'yan damfara da Najeriya ta yi zuwa ƙasashensu
20/10/2025 Duración: 10minMahukunta a Najeriya sun tasa ƙeyar ƴan asalin ƙasashen waje su 192 da aka tabbatar da sun shahara wajen aikata damfara ta yanar gizo a cikin ƙasar. Mutanen waɗanda aka kama a birnin Lagos, sun haɗa da China, Philippines, Malaysia, Pakistan, Tunisia da dai sauransu, waɗanda tuni kotu ta tabbatar da laifukansu. Shin me za ku ce a game da yadda ƴan damfara a yanar gizo ke neman mayar da Najeriya a matsayin tunga domin baje kolinsu? Shin ko kun gamsu da irin matakan da mahukunta ke ɗauka domin daƙile wannan matsala? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan yajin aikin malaman jamio'i a Najeriya
14/10/2025 Duración: 10minA Najeriya yajin aikin malaman jami’o’i ya shiga rana ta biyu, lamarin da tuni ya fara haifar da cikas musamman ga ɗalibai da mafi yawansu na tsakiyar zana jarrabawa. Yayin da ƙungiyar Malaman ASUU ta ce ta shiga yajin aikin ne domin neman gwamnati ta cika aiwatar da yarjejeniyar da ɓangarorin biyu suka rattaba wa hnnu tun 20009, yayin da a gwamnati ke cewa tuni aka aiwatar da abubuwan da kunshe a yarjejeniyar. Shin ko yaya ku kallon wannan yajin aiki? Wace shawarar za ku bai wa bangarorin biyu domin gaggauta wannan saɓani da ke tsakaninsu. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan afuwar da shugaban Najeriya ya yiwa wasu mutane 175
13/10/2025 Duración: 10minRa’ayoyi na ci gaba da bayyana dangane da afuwar da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi wa mutane 175 da aka kama da laifuka daban daban. Daga cikin waɗanda aka yi wa afuwar har da waɗanda aka yankewa hukuncin kisa, da safarar makamai da miyagun ƙwayoyi da dai sauransu. Shin ko me za ku ce a game cancanta ko kuma rashin dacewar yin wannan afuwar? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta
10/10/2025 Duración: 10minKamar yadda aka saba, a kowace ranar Juma'a, sashen Hausa na RFI na baiwa masu sauraro damar tofa albarkacin bakinsu kan batutuwan dake ci musu tuwo a ƙwarya, kama dag siyasa, zamantakewa, tattalin arziƙi da dai sauransu. A yau ma bamuyi ƙasa a gwiwa ba wajen baku wannan dama. Idan kuka latsa alamar sauti, zakuji mabanbanta ra'ayoyi a shirin da Abida Shu'aibu ta gabatar...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan zaɓen shugaban ƙasar Kamaru
09/10/2025 Duración: 10minA ƙasar Kamaru, yanzu haka ana ci gaba da yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar da za a yi ranar lahadi mai zuwa, inda ƴan takarar 9 za su fafata da shugaba mai-ci wato Paul Biya. Kawo yanzu dai yaƙin neman zaɓen na gudana a cikin kwancin hankali, yayin da tuni mahukunta suka yi gargaɗi domin kauce wa duk wani abu da zai iya haifar da matsala a wannan marra. Shi me za ku ce a game da wannan zaɓe da ake shirin gudanarwar a Kamaru? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan ranar Malamai ta Duniya
06/10/2025 Duración: 09minA jiya ne aka gudanar da bikin ranar malamai ta duniya cikin yanayin ƙuncin rayuwa da ƙarancin albashi, musamman a wasu ƙasashen Afirka da malaman ke ɗanɗana kuɗarsu. An ware wannan rana ne, domin nuna goyon baya ga irin gudunmawar da suke bayarwa ga ci gaban rayuwar al’umma a fannoni da dama. Wanne hali malamai ke ciki a yankunanku? Shin kun gamsu da irin gudunmawar da suke bayarwa a yankunanku. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Ku latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
-
Tattaunawa da masu saurare kan bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ƴanci
01/10/2025 Duración: 09minShirin 'Ra'ayoyin Mai Saurare' na wannan rana tare da Abida Sha'aibu ya tattauna ne kan bukin cika shekaru 65 da samun ƴancin Najeriya daga turawan mulkin mallakar Burtaniya da aka gudanar a wannan Laraba, wato tunawa da ranar 1 ga watan Oktoban shekarar 1960, kan halin da ƙasa ke ciki ta fannin ci gaba ko kuma koma-baya a tsawon waɗannan shekaru.
-
Ra'ayoyin masu saurare game da dambarwar ƙungiyar PENGASSAN da Ɗangote
30/09/2025 Duración: 09minA Najeriya ana ci gaba da kai ruwa rana tsakanin matatar Dangote da kungiyar manyan ma’aikatan man fetur da iskar gas wato PENGASSAN. Tun daga lokacin da matatar Dangote ta fara aiki kawo yanzu, an samu takaddama irir-iri daga kungiyoyin da ke da alaka da man fetur da kuma iskar gas. Ko me yasa takun saka tsakanin Dangote da masu ruwa da tsaki a harkar mai, yaki ci yaki cinyewa? Me ku ke ganin ummul aba’isin wannan dambarwa da take bullowa daga kusurwa-kusurwa, wanda ake ganin zai haifar da tashin farashin mai a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai........ Ku latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyin na ku.....................
-
Ra'ayoyin masu saurare game da yaƙin neman zaɓen Kamaru
29/09/2025 Duración: 10minAn ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar Kamaru, inda mutane 12 ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya za su kara da juna a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu. Yayin da Paul Biya ke fatan sake samun yardar al’umma don ci gaba da mulki karo 8, a nasu ɓangare kuwa 'yan adawa na kallon zaɓen a matsayin wata dama don samar da sauyi a ƙasar. Shin me za ku ce a game da wannan yaƙin neman zabe? Ko wane fata ku ke yi wa al’ummar Kamaru? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin....
-
Ra'ayoyi kan shirin Amurka na hana ƴan Najeriya masu rashawa shiga ƙasar
25/09/2025 Duración: 09minShirin Ra'ayoyin mai Saurare na wannan ranar Alhamis 25 ga watan Satumbar 2025, wanda Oumar Sani ya gabatar, ya tattauna ne kan matakin gwamnatin Amurka na hana duk wani ɗan Najeriya ciki har da jami’an gwamnati da aka samu da hannu da rashawa bisar da za ta ba su damar shiga ƙasar.
-
Ra'ayoyin masu saurare kan ficewar ƙasashen AES daga kotun ICC
24/09/2025 Duración: 10minBurkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewa daga Kotun Hukunta Laifuka ta Duniya da ke birnin Hague, bisa zargin kotun da kasancewa ƴar amshin ƴan mulkin mallaka. To sai dai wasu na ganin cewa shugabannin ƙasashen uku sun ɗauki matakin ne don kauce wa bincike ko tuhuma daga wannan kotu. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacinku a yau cikin shirin na Ra'ayoyinku masu saurare. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan ɗage haramcin shigar da siminti a Nijar
22/09/2025 Duración: 10minGwamnatin Jamhuriya Nijar ta ɗage haramcin shigar da siminti a ƙasar, sakamakon yadda ake fama da ƙamfarsa, lamarin da ya haifar da tsadarsa a kasuwa. Wani lokaci a can baya ne dai mahukunta suka sanar da haramta shigar da simintin don kare kamfanonin da ke sarrafa shi a cikin gida, amma kuma aka wayi gari na cikin gidan sun gaza wadatar da masu buƙatar sa domin yin gini. Shin ko me za ku ce a game da cire haramcin? Wannan shine maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwan dake ci musu tuwo a ƙwarya
19/09/2025 Duración: 10minYau juma'a, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar faɗin albarkacin bakinsu, kan batutuwan dake ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tattalin arziƙi, ilimi, lafiya, zamantakewa, siyasa da dai sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare Nasiru Sani...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan umarnin gwamnatin Neja na duba khuɗubobi kafin yaɗa su
18/09/2025 Duración: 10minA Najeriya, gwamnatin Neja ta umarci ilahirin limaman masallatan Juma'a a faɗin jihar da su riƙa miƙa mata bayanan da ke ƙunshe a cikin huɗubar da za su gabatar don tantancewa, matakin da Gwamna Muhammadu Umar Bago ke cewa yunƙuri ne na kaucewa duk wata barazana ta cusa ƙiyayya ko kuma haddasa rikici da malaman ka iya yi. Yaya kuke kallo wannan mataki na Gwamnan jihar Neja? Shin kuna ganin akwai buƙatar shigowar gwamnati don daidaita yadda malamai ke gudanar da khuɗubobi da sauran karatuttuka? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Ku latsa alamar sauti domin sauraren shirin....
-
Ra'ayoyin masu saurare game da yadda ICPC ke sanya ido kan kuɗaɗen ƙananan hukumomi
17/09/2025 Duración: 10minHukukumar Yaƙi da Rasha ta ICPC a Najeriya, ta ce yanzu haka tana ƙara sa-ido dangane da yadda ake kashe kuɗaɗe mallakin ƙananan hukumomi a ƙasar. Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da gwamnatin tarayya ke shan matsin lamba domin ganin ta aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli wanda ya buƙaci a zuba wa ƙananan hukumomin kuɗadensu kai-tsaye a maimakon bi ta hannun gwamnonin jihohi. Ko me za ku ce a game da jan ƙafa wajen aiwatar da wannan umarni da kotu ta bayar tun watan Yulin shekara ta 2024 da ta gabata? Wace irin rawa ya dace ICPC ta taka don kare dukiyar ƙananan hukumomi a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakin ku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...
-
Ra'ayoyin Masu Sauraro kan janye yajin aikin Likitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya
15/09/2025 Duración: 09minShirin Ra'ayoyin Mai Sauraro na wannan Litinin tare da Nasiru Sani ya tattauna ne kan janye yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyar da ƙugiyar likitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya ta sanar a ƙarshen mako, kwanaki bayan fara ta a ranar Juma'ar da ta gabata, inda ta ƙara wa'aɗin makwanni biyu don a biya musu buƙatunsu. Daga cikin buƙatun ƙungiyar da take nema gwamnati ta biya akwai abinda ya shafi albashi da alawus-alawus da kuma walwalar mambobinta. Ku latsa alamar sauti domin sauraron ra'ayoyin wasu daga cikin masu sauraro da suka aikoma ta manhajarmu ta Whatsapp
-
Ra'ayoyin masu saurare kan matakin Najeriya na haramta zirga-zirgar jiragen ruwa marasa lasisi
11/09/2025 Duración: 09minA yunƙurin rage yawaitar haɗura akan ruwa, Hukumar Kula da Zirga-zirga a kan Kogunan Najeriya ta haramta yin amfani da jiragen ruwa a kan kogunan ƙasar sai tare da samun izini daga gare ta. Wasu daga cikin matakan da hukumar ta sanar sun haɗa da hana yin lodin fasinja sai a tashoshin da ta amince da su, sai tilasta wa fasinja yin amfani da rigar kariya, da mallakar takardar shaidar ƙwarewa ga illahirin matuƙan jiragen da dai sauransu. Anya waɗannan matakai za su taimaka don rage afkuwar haɗurra a kan kogunan Najeriya? Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani.
-
Ra'ayoyin masu saurare kan ƴancin faɗar albarkacin baki a Nijar
10/09/2025 Duración: 08minA Jamhuriyar Nijar, batun ƴancin faɗin albarkacin baki, aikin jarida ko kafa ƙungiyoyi da sunan yi fafutuka na ci gaba da fuskantar barazana. Bayan rusa ilahirin jam’iyyun siyasa, daga bisani an ci gaba da kama ƴan jarida da masu fafutukar kare hakkin bil adama, tare da jefa ƙungiyoyin kwadago a cikin fargaba ta hanyar farawa da rusa kungiyoyin alƙalai na ƙasar. Ku latsa alamar sauti don jin ra'ayoyin jama'a kan wannan batu.
-
Ra'ayoyin masu sauraren kan rikicin NUPENG da Dangote a Najeriya
08/09/2025 Duración: 10minA Najeriya, an shiga takun-saƙa tsakanin Ƙungiyar NUPENG ta direbobin motocin dakon mai da iskar gas da kuma Ɗangote wanda ya sanar da sayo motoci dubu 4 da zai yi amfani da su don rarraba man fetur a sassan ƙasar. Yayin da NUPENG ke cewa magoya bayanta ne ke da hurumin raba mai da iskar gas a ƙasar, sai dai manazarta na cewa Ɗangote, na da damar raba hajarsa sakamakon sakin mara da aka yi wa ɓangaren kasuwanci a ƙarƙashin dokokin Najeriya. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi....
-
Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa daban-daban
05/09/2025 Duración: 10minKamar yadda aka saba kowacce ranar Juma'a mukan baku dama don bayyana mana ra'ayoyinku game da batutuwa daban-daban da suka shafin fannonin rayuwa daban-daban don kira ga masu ruwa da tsaki da su kawo ɗauki. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Hauwa Aliyu Garba