Lafiya Jari Ce
An gudanar da gangamin wayar da kai akan cutar daji a Jamhuriyar Nijar
- Autor: Vários
- Narrador: Vários
- Editor: Podcast
- Duración: 0:10:05
- Mas informaciones
Informações:
Sinopsis
Kowanne watan Oktoba, lokaci ne da ɓangarorin lafiya a Jamhuriyyar Nijar ke amfani da shi wajen gudanar da gangamin wayar da kai a ƙasa baki ɗaya game da cutar sankara ko kuma Cancer wadda ake ganin ƙaruwar masu kamuwa da ita a sassan wannan ƙasa ta yankin Sahel,,,, wannan shi ne maudu’in da shirin na Lafiya jari ce zai mayar da hankali akai sai ku biyomu. Jamhuriyyar Nijar na ganin sabbin kamuwa da cutar ta cancer dubu 9 da 787 duk shekara ciki kuwa har da mata masu kamuwa sankarar mama dubu 2, wanda ke matsayin wani ɓangare na jumullar mata miliyan 2 da dubu 300 da ke kamuwa da sanakarar maman duk shekara a sassan duniya bisa alƙaluman hukumar WHO.