Ilimi Hasken Rayuwa

Yadda dokar rage kuɗin makaranta za ta yi tasiri ga tsarin Ilimi a Nijar

Informações:

Sinopsis

Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali ne kan dokar da ta tilastawa makarantu masu zaman kansu rage kudin makaranta da gwamnatin Nijar ta kafa, wanda ke zuwa bayan ƙarin hutun makarantu na makwanni biyu saboda mamakon ruwan a ƙasar ta yankin Sahel. Ƙarƙashin wata doka da shugaban gwamnatin Sojin Nijar Abdourraham Tchiani ya sanya hannu ce ta buƙaci dukkanin makarantun su rage kuɗin da suke karɓa da kashi 20, kodayake wannan doka bata shafi makarantun da ke karɓar kuɗin da bai kai CFA jaka hamsin ba. Tuni iyaye suka yi maraba da wannan mataki. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.